Kungiyar Hadin Kan Musulunci

Kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta yi Allah wadai da harin ta'addanci da aka kai a yammacin Nijar

Jeddah (UNA)- Kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC ta yi Allah wadai da harin ta'addanci da wasu 'yan bindiga suka kaddamar a yammacin jamhuriyar Nijar, wanda ya lakume rayukan fararen hula da dama da suka hada da mata da kananan yara. Kungiyar ta sake sabunta matsayar ta na yin Allah wadai da ta'addanci a kowane fanni, tare da tabbatar da cikakken goyon bayanta ga mahukunta a Jamhuriyar Nijar a yakin da suke da ta'addanci da tsattsauran ra'ayi. Babban sakataren kungiyar Dr. Youssef bin Ahmed Al-Othaimeen, ya jajantawa iyalan wadanda lamarin ya shafa da gwamnati da al'ummar Nijar. (Na gama)

Labarai masu alaka

Je zuwa maballin sama