Jeddah (UNNA) – Babban Sakatariyar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Musulmi ta OIC ta yi Allah wadai da harin da aka kai da makamai a ginin Attaché na kasar Libiya a birnin Khartoum na kasar Sudan.
Sakatariyar Janar din ta yi Allah-wadai da hare-haren da ake ci gaba da kaiwa kan gine-ginen diflomasiyya a birnin Khartoum tare da jaddada wajibcin mutunta alfarmar gine-ginen diflomasiyya da kuma kiyaye yarjejeniyoyin kasa da kasa musamman yarjejeniyar Vienna kan huldar diflomasiyya.
(Na gama)