
Geneva (UNA/QNA) – Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya (UNHCR) ta bayar da rahoton cewa, rikicin kasar Sudan ya kasance mafi girma da aka fi sani da ‘yan gudun hijira a duniya, inda mutane miliyan 12 suka rasa muhallansu, ta kuma bayyana cewa dubban iyalai na ci gaba da tserewa daga El Fasher da Darfur.
Kakakin ofishin kula da ayyukan jin kai na MDD OCHA Jens Laerke ya bayyana cewa, miliyoyin 'yan kasar Sudan na matukar bukatar taimako, kana ana kashe fararen hula da ma'aikatan agaji ba tare da wani hukunci ba, kuma ana samun yawaitar cin zarafin mata.
Ya yi kira da a tabbatar da samun damar kai agaji cikin aminci, da kuma ba da kariya da tallafawa kungiyoyin cikin gida.
Sean Hughes, jami'in hukumar bada agajin gaggawa ta MDD kan rikicin kasar Sudan, ya bayyana mummunan halin da ake ciki a kasar Sudan a matsayin mafi girman matsalar jin kai a duniya, ta kowacce fuska, inda kimanin mutane miliyan 25, ko rabin al'ummar kasar ke fuskantar matsananciyar yunwa, da kuma yara kusan miliyan biyar da mata masu fama da matsananciyar yunwa.
(Na gama)



