
Geneva (UNA/WAS) – Wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman mai kula da yara da rikice-rikice, Vanessa Fraser, ta yaba da ci gaban da aka samu wajen kare yara a Syria.
Ta yi marhabin da sake jaddada aniyar Syria kan yarjejeniyoyin kasa da kasa na kare yara, inda ta yi kira ga dukkan bangarorin da su saki yara kanana, tare da yin kira ga kasashen duniya da su goyi bayan wannan kokarin tare da hadin gwiwar MDD.
(Na gama)



