Porto-Novo (UNA) - Cibiyar Nazarin Tsaro a Benin ta shirya wani taron bita a kwanakin baya, wanda ya samu halartar kwararrun kafofin yada labarai da wakilan kungiyoyin fararen hula, wadanda suka koyi mafi kyau da sababbin hanyoyin da za a yi don hanawa da kuma magance tashin hankali. Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na cibiyar Muryar Hikima, wata kungiya mai alaka da kungiyar hadin kan kasashen musulmi, taron na da nufin taimakawa kasar Benin daga barazanar ta’addanci da kuma koyi da abubuwan da wasu kasashe suka samu a wannan fanni. ((Na gama))
kasa da minti daya



