Yamai (UNA)- Shugabannin kasashen G5 Sahel da Faransa da kuma shugaban hukumar Tarayyar Afirka sun amince da nada shugaban kasar Nijar Mohamed Bazoum a matsayin mai shiga tsakani a rikicin siyasar kasar Chadi, bayan rasuwar shugaba Idriss Deby Itno. Kamfanin dillancin labaran Niger ya bayar da rahoton cewa, an dauki wannan mataki ne a wani taro da aka gudanar a ranar Juma'ar da ta gabata, a gefen jana'izar Marshal Idriss Deby Itno na kasar Chadi. (Na gama)
kasa da minti daya



