Kuwait (KUNA)- Ma'aikatar harkokin wajen Kuwait a yau Talata ta yi marhabin da rahoton da kwamitin bincike na kasa da kasa mai zaman kansa na Majalisar Dinkin Duniya ya fitar, wanda ya tabbatar da cewa irin wahalhalun da al'ummar Palastinu ke yi a zirin Gaza da sojojin haramtacciyar kasar Isra'ila ke yi ya zama wani gagarumin kisan kare dangi.
A cikin wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ta bayyana cewa, wannan rahoto ya tabbatar da ko shakka babu irin mugun nufi da sojojin mamaya na haramtacciyar kasar Isra'ila suke da shi na aiwatar da manufofin da suke da nufin lalata al'ummar Palastinu bisa tsari.
Ta ce kasar Kuwait tana sake yin kira ga kasashen duniya da kwamitin sulhu da su gaggauta daukar matakin dakatar da wannan kisan kiyashi, da samar da kariya ga fararen hula da ba su ji ba ba su gani ba a yankunan Falasdinawa da ta mamaye, da kuma dorawa mahukuntan kasar alhakin keta dokokin kasa da kasa da dokokin jin kai na kasa da kasa, tare da tabbatar da cewa ba za su tsira daga azaba ba.
(Na gama)



