
Paris (UNA/WAFA) – Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya fada a ranar Litinin cewa ba za a amince da harin bam da Isra’ila ta kai a wani asibiti a Gaza, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula da ‘yan jarida.
A jiya ne dai sojojin mamaya na Isra'ila suka kai harin bam a cibiyar kula da lafiya ta Nasser da ke Khan Yunis a kudancin zirin Gaza, inda suka kashe fararen hula akalla 20 da suka hada da 'yan jarida biyar.
(Na gama)



